SANADIN LABARINA 31

 


 Page (31)

ASSALAM ALAIKUM DEARIES

BARKAN KU DA KOKARI…. KAMAR

KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA

MUNA BARAR ROKON KU WAJEN

TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS

DAKE MANHAJAR YOUTUBE

YARO NE DAYA TASHI DA SON

KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE

KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN

SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A

TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE.

A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A

TEMAKA DA SHARING MA... JAZAKUM

ALLAH KHAIRAN AS YOU DO... "

Assalamualaikum dear sisters and

brothers.

Welcome to ummu sudais YouTube

channels?

A channel where the Holv Quran is been

recited from different Angles.

Click on this link and listen to the

Beautiful recitation that will melt your

heart

https://youtu.be/Lafgc749sK8

Your subscription to our channel is of

Great important. Please help us grow

our channel by subscribing and liking 




****

   Da sauri ta bud'e motar ta fice ya tsaya yana kallon ta, hadda d'an gudun ta, ta bude kofa sai ta waigo ta kalli wajen da yake, ta jujjuya bakin ta sannan ta shige da sauri, murmushi yayi ya rufe motar ya nufi bangaren Maman yana jin sa sakayau kamar wanda ya sauke wani baban nauyi dake kansa. A tsaye ya samu Maman tana kaiwa da komowa a tsakanin hadadden falon nata, tun kafin ya gama shigowa ta soma fada


"Ni zaka wulakanta Tariq? Ni?"


"Mama... Me ya faru?"


"Tambaya ta kake me ya faru? Baka san me ya faru ba Tariq?"


Girgiza kai yayi


"Allah Mama ban sani ba."


"Menene hadin ka da yarinyar nan?"


"Mama?" 


"Eh menene hadin ka da ita? Daga ina kuke ma tukunna? Kar dai kace min? Noo ba zai yiwu ba."


"Dan Allah ni dai Mama ki kwantar da hankalin ki."


"Ya zan kwantar da hankali na wai? Hu? Taya kake so na kwantar da hankali na ina ganin ku tare? Kasan abinda hakan ke nufi? Na rasa ka kenan,."


"Ba zai lasting ba mama, just give me sometime, bana so akai na ku samu matsala da Baba."


_"I'm doing it for Baba."_  Ya fadawa kansa da kansa k'asa-k'asa amma sai yaji kamar zuciyar sa bata karbi uzurin sa ba, so yake dole ya karfafa kansa cewa duk ma abinda yake saboda a samu maslaha a tsakanin iyayen sa ne, shi he has nothing to do with her, ba daidai dashi bace sai ya karyarta ma ai, amma kuma sam zuciyar sa taki bud'e masa kofar da zai aje irin wannan uzurin da har zai samu wajen zama a cikin zuciyar tasa


"Don't go far na gaya maka toh,  Halima da yarinyar are cunning, idan baka yi wasa ba you will end up..."


"Nooo Mah..." Ya katse ta


 "I don't think hakan zai faru, in sha Allah hakan ma ba zai faru ba."


"I hope so, fita zan amma ganin ku tare na ji ma na fasa, we only have few days sai kayi duk yadda zakayi kafin a shiga cikin bikin, bana son kuma silly excuse dan ba zan karba ba."


"In sha Allah." Yace amma kuma sai yake jin kamar ba zai iya aikata abinda Maman take so ba, amma kuma why not? Shi ai ba son yairnyar yake ba.

 Fita yayi ya nufi bangaren su, yaje yayi wanka sannan yayi breakfast ya zauna yana hutuwa a falon har Fauwaz ya shigo.


***Kamar munafuka haka ta shiga part din nasu, aunty na zaune a falon taji kamar ta nutse saboda tsabar kunya, kanta a k'asa ta shiga ciki, ta gaida Auntyn tayi saurin shigewa dakin ta, tasa key ta kwanta rigingine tana kallon pop, ta kasa tantance yanayin da take ciki gaba daya,ta kuma rasa a wanne mataki zata ajiye abinda Ya Tariq din yayi, tunda ya nuna mata time kawai yake jira yayi ending marriage din nasu, kila dai kawai so yake ya dagula mata lissafi ya barta da ciwo a zuciyarta, zatayi duk yadda zatayi ba zata sake bari su hadu ba, ballantana har wani abu makamancin hakan ya faru. Message ne ya shigo wayar ta sai a lokacin ta tuna da wayar, baki daya kamshin turaren sa take kamar wadda tayi wanka da ruwan turaren, duk ya cika mata kofofin hancin ta, wayar ta dauko ta shiga message din sai taga Ya Fauwaz ne


_"I will take over daga nan, kamar yadda nayi miki alkawari Ya Tariq sai yazo da kansa ya kawo kansa wajen ki, ki barmun komai, ke dai kawai kiyi avoiding nasa."_


Murmushi tayi kawai ta goge text din, dan ita bata taba tunanin Tariq din zai yi abinda Fauwaz din yace ba, bata ki ba idan baya hayyacin sa ko kuma dai wani babban al'amari, itama tun farko tayi gangancin hada kanta dashi, banbancin su yayi yawan da zai yi wuya ya iya sakkowa zuwa level dinta. Har magriba tana kunshe a daki sau biyu Amira na zuwa suje wajn Yaya amma kemaimai taki, gobe za'a kawo musu ragowar wasu kayan kamshi na turara jiki wanda na kwana uku ne kachal zaa musu daga nan zaa shiga hidimar bikin wanda bata dauke shi yanzu da muhimmanci ba dan bata san matsayin ta a wajen wanda ake yi domin shi ba.

   Da safe Amira tazo su tafi wajn Yayan da k'yar sai da Aunty ta bata rai sannan ta amince amma da cewa tayi ba zata ba ta daina zuwa, duk da Amira tasan dalilin amma basu taba maganar ba dan jidda zurfin cikin ta yayi masifar yi mata yawa, ganin bata fada mata ba yasa ta ki mata maganar gaba daya.

   Ita aka farawa dan Ya Safiyya da Umaima basu ma tashi ba, ana gama mata ta sulale ta koma nasu part din dan tayi alkawarin ba zata yarda su hadu ba. Tana shiga Aunty ta tashi tana rike bakin ta kamshin irin mayatataccen kamshi ne me dadin gaske, kudi sosai aka kashe dan ita kanta daga wani state din tazo matar bayan wacchan ta gama musu ta tafi.


"Kinji kamshin da kike Jidda?"


Kunya ce ta kamata, ta rufe fuskar ta, da tafin hannun ta tana dariya, kod'a ta Aunty ta dinga yi ita dai kawai dariya take cike da kunyar Auntyn dan abinda ya faru jiya.


***Kwana biyu bayan sun dawo yana ta zuba ido babu ita babu alamar ta, sau wajen uku yana zuwa part din Yaya amma sai ya tarar bata nan, har sai da Yaya ta gaji tace wai lafiya yake mata safa da marwa a gida ne? Fita yayi kawai be sake dawowa ba, chan anjima ya tafi wajn Auntyn amma sai suka hadu da Auntyn a hanya zata fita, ya juya bayan sun gaisa ya samu waje ya zauna yana saka ido ko zai ga fitowar ta amma shiru har dare babu ita babu alamar ta. Be san dalilin da yasa ya damu da son ganin ta ba, shi dai kawai yaji yana so ya ganta ko ma ba zata masa magana ba. Kamar ya koma wajen Auntyn amma sai ya hakura ya fasa. Da safe ya sake saka ido amma shiru, a lokacin ne kuma gidan nasu ya fara cika da mutane, yawanci yan uwan Mama ne suka fara zuwa a ranar, silalewa yayi ya bar gidan dan baya son su ganshi kwata-kwata. 

  

***Suna zazzaune dukka yan matan a falon farko su kuma su Mama na ciki, Salma ce tace tambaye Maryam 


"Wai Ya Tariq baya nan ne?"


"Wa? Ya Tariq din zaki tambayen? Wallahi ban san in da yake ba."


"Har yanzu Ya Tariq baya son mutane, wallahi na matsu na ganshi naga yadda ya chanja."


"Ganin Ya Tariq sai kin cika Form, da dai Jiddaa ce." Amira tace tana dariya, bata fuska Salma tayi, taja tsaki tana mikewa


"Sai ana maganar mutane kuna kawo mana maganar wata chan dan Allah."


"Kinyi maganar mijin ta ai dole ayi maganar ta."


"Wai miji, tab!" Ta kwashe da dariya


"Kina mamaki ne?"


"Ba dole ba, dan Allah me ya Tariq zai ci da yarinyar nan? Yarinyar da aka taimakawa aka mayar mutum sai shegen girman kai ita ba yar uban kowa ba."


"Aiko baki san jiddah ba."


"Bana son ma na santa."


"Toh gaskiya ki bar maganar nan kar ma taji wallahi, kinga abinda kika taba yi mata din nan."


"Ai ku kome za'a ce akanta bakwa gani, sai kuyi tayi."


Turo kofar yayi, ya shigo fuskar sa a tamke,ya dan ji maganganun da suke sama-sama ya kuma fuskanci abinda suke magana akai, shi yasa ya tsani taron mata dan babu yadda za'a yi su hadu su tashi ba su tada fitina ba. Gaishe su sukayi a kusan tare duk sun rude Allah yasa be ji me suke cewa ba, be amsa ba yayi wucewar sa dan dama Mama ce tace yazo ya gaida su Aunty Nafi dasu Aunty Mimi, da ba dan haka ba, da ba zai shigo ba. A tsaitsaye ya gaishe su, ya fito yazo zai wuce Salma tayi tsagal tace


"Ya Tariq ina wuni?" 


Ko kallon in da take be ba, yayi ficewar sa, yana fita su Ummi suka kwashe da dariya, kamar ta kurma ihu haka taji dan kunya. Dama Aunty Nafi ce ta saka ta, tace tayi kokarin shige masa,amma dan wulakanci ko gaisuwar ta be amsa ba bare tasa ran zai kalli in da take. Tsokanar ta suka dinga yi ta rasa ina zata saka kanta sai daki ta gudu saboda borin kunya.

  

***Shi baki daya baya jin dadin zaman gidan, a matukar takure yake gaba daya da zaman waje dayan gashi ba wani sanin wurare yayi a garin ba dan ma dai yana da saurin gane waje kuma yanzu an cigaba akwai map, gashi Baba yace dole sai ya kara wasu satittikan kafin ya tafi, Mama kuma ta saka shi a gaba tana so taji ya ake ciki, gashi ya rasa yadda zai ko wulgawarta baya gani sau biyu da aunty tana part din Baba yana zuwa ya murda kofar dakin ta amma a rufe zai ji, baya kuma magana yake juyowa dan baya son ta raina shi ko taga kamar ya damu da ita ne, so yake kawai yaga ta daina kukan ko har yanzu tana yi? Gashi ya rasa solution bayan yayi mata alkawari itama, gashi zuciyar sa ta hana shi kemaimai da ya fara tunanin yadda zai yi sai kawai yaga ta fara hasaso masa Jiddan.

   Wajen Yaya ya nufa duk da itama jama'ar ta sun fara zuwa, wanda dama duk suna burin zuwa Abujan sai kawai Baba yayi amfani da damar nan aka ce duk me son zuwa ya shirya, aikuwa suka dinga tururuwa kafin kace me gidan dame d'am da mutane. Tun a kofar shiga yaji hayaniya sai fasa shiga ya bari idan dare yayi ya dawo.

     Da daddare Baba ya dawo ya kirashi suka zauna yace menene shirin sa akan tarewar jiddaa, shiru yayi yana nazari har sai da Baban ya sake maimaita masa sannan yace duk yadda akayi yayi, dan jim Baban yayi da zai ce wani abu sai kawai ya fasa


"Shikenan, sai ka fara shiri, akwai gidan da zaku zauna, Incase ko baka nan dai muna kusa."


"Nagode Baba, Allah ya kara girma."


"Amin ya Allah, dan Allah Tariq karka wulakanta min 'ya, Dan Allah."


"In sha Allah."


"Kuma inaso kuje kai da ita ku gaida mahaifin ta, sai ka saka muku rana bayan sun gama bidi'o'in nasu na mata."


"In sha Allah zamuje."


"Shikenan Allah yayi muku albarka."


"Amin ya Allah."


***Duk yadda Mama taso Tariq ya yi botsare akan maganar auren nan sam yki, ta ma kasa gane in da ya dosa kwata-kwata, kamar ma so yake kawai ta kwantar mata da hankali shiyasa ma yake biye mata da nuna mata shi ma baya son abun. Babu yadda za'a yi baya so kuma ya hakura har a kawo yanzu, wanda nan da kwana biyu zata tare daga nan kuma bata san ya zai yi ba. Yanayin hayaniyar bikin da dumbin mutanen da suka taru yasa ta hakura da maganar ba wai dan ta hakura gaba daya ba, yanzu zatayi focusing kawai akan su Safiyya idan aka gama zata dawo kan Tariq din ne dan ba zata yarda a lalata mata rayuwar dan ta ba.

  Baki daya gidan idan ka cire bangaren Yaya kowa ya yi shirin tafiya wajen hadaddiyar dinner din da aka shirya, Mama bata nan sun fita da Aunty Mimi daga chan zasu wuce ita da wata babbar kawarta da suka hadu a taron da suke na matan ministoci. Su jidda na wani babban gidan makeup ita da su Ya Safiyya wadda da k'yar akayi convincing dinta ta yarda zaa mata amma yar kad'an dan bata son irin heavy makeup din, ita kadai take budirin ta dan me gayya me aikin kamar ma be san anayi ba, shiyasa Amira zata tsayata su tafi tare driver ya kaisu su kuma Ya Safiyya miijin kowacce ne zaizo su tafi abun su. Su Umaima ne suka fara tafiya sai Ya Safiyya ma ta tafi ya zama sai su kadai dama kuma sune karshen gamawa. Driver Amira ta kira tace sun gama ya matso da mota, yace mata ya dan fita daga cikin wajen zai shigo da Oga yana waje. Yana cewa oga ta gane Ya Tariq yake nufi dan haka yake ce musu shi da Ya Fauwaz dan dama ba bahaushe bane ba. Kin fadawa jiddah tayi sai da ya dawo ya kira sannan tace su taso su tafi.


   Yana tsaye jikin sabuwar motar sa, wadda Baba ya bashi gift dinta jiya na kammala karatun sa da kuma aure, kaftan ne a jikin sa fari me hade da navy blue collar da jikin hannun, takalmi da hular kansa duk navy blue ne,dinkin da kad'an ya wuce guiwar sa. Kallon wajen yake a tsanake har suka fito, Amira ta hango shi suka nufi wajen da yake a tsaye, sai da suka kusa karasawa sannan Jidda ta ganshi, tsayawa tayi chak cike da mamakin ganin sa, juyowa yayi suka hada ido ya tako ya same su a wajen da suke tsaye


"Kije Sam ya ajiye ki,mu ba zamu je dinner din ba."


"Ok." Amira tace tayi gaba da sauri, 


"Muje ko?" Yace yana nuna mata hanya


"Tafiya zamuyi da Amira fa." Ta fada idon ta nayi raurau kamar zatayi kuka


"Na sani ai, cewa nayi ba zaki je ba, babu wata dinner da zaki oya shiga mota mu wuce gida."


"Dan Allah ka barni naje."


"Ba zaki ba."


"Dan Allah." Ta sake cewa already har ta soma kukan bakin ciki, kukan ka gama saka rai a abu ace ba zaka ba, da tun farko da tace ba zata ba da sun kyale ta shikenan, amma sai da ta hakura har tazo make up sannan yace ba zata ba..


"Oya, muje ko na daga sama, kinsan kuma zan iya."


Waigawa tayi ta hango wasu saurayi da budurwa a chan gefen su, ta sake waigawa dayan barin shima wasu ne a zaune suna hira, sai kawai ta nufi motar tana had'a hanyaa.

[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**


      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

Previous Post Next Post
Sponsored Links
Sponsored Links